Kotun zaɓen shugaban ƙasa ta ɗage zama zuwa Talata don jin ƙorafin PDP

 Kotun zaɓen shugaban ƙasa ta ɗage zama zuwa Talata don jin ƙorafin PDP

Kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya da ke zamanta a Abuja ta ɗage zamanta zuwa gobe Talata domin sauraron ƙorafin babbar jam'iyyar adawa ta PDP, da ɗan takararta Atiku Abubakar, da kuma jam'iyyar APM.

Hukumar zaɓen ƙasar INEC ce ta ayyana ɗan takarar jam'iyyar APC Bola Ahmed Tinubu a matsayin wanda ya yi nasara da ƙuri'a miliyan 8,794,726, bayan da ya kayar da manyan abokan takararsa Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP.

Bayan da suka yi watsi da sakamakon zaɓen Atiku da Obi sun nufi kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen don ƙalubalantar nasarar Tinubun.

A zaman sauraron ƙorafe-ƙorafen da ta fara ranar Litinin, kotun ƙarƙashin jagorancin mai shari'a Haruna Tsammani ta alƙawarta yin adalci ga duka ɓangarorin da ke cikin shari'a.

Comments

Popular posts from this blog

Real Madrid za ta kara da Man City a Champions League