Posts

Showing posts from April, 2023

A zamanin Iyaye da Kakanni ba su dauki Kishiya a Matsayin Abokiyar gaba ba, sun Dauke ta ne a Matsayin Abokiyar rayuwa kuma Abokiyar Shawara

Image
 “A zamanin Iyaye da Kakanni ba su dauki Kishiya a Matsayin Abokiyar gaba ba, sun Dauke ta ne a Matsayin Abokiyar rayuwa kuma Abokiyar Shawara, Sa6anin Matan Yanzu da wasu kan Kashe Aurensu kawai don za a musu Kishiya, Wannan Kuskure ne ya kamata mu kalli Tsarin Rayuwar Magabatanmu.”

Yadda zaki sami fata mai kyau: Idan kikabi wa innan Hanyoyin inshaAllah zaki ga chanji a fatar ki.

Image
 Yadda zaki sami fata mai kyau: Idan kikabi wa innan Hanyoyin inshaAllah zaki ga chanji a fatar ki. 1. Yawan shan ruwa kamar 6-8 cups a rana. 💧 2. yawan shafa mai kar a ringa bari jiki yna bushewa. 3. A ringa exploiting skin da natural scrub sau 1-2 a sati. 4. ki ringa amfani da natural oil kamar su olive oil, coconut oil, Shea butter: idan kina so jikinki ya ringa taushi ki ringa amfani da man olive oil da Shea butter. 5. kar a kwanta da makeup: ki tabbata kin Wanke fuskar ki sosai ko kiyi amfani da coconut oil da tissue wajan cire makeup. 6. A daina amfani da cosmetics din da sukai expire. 7. Sannan a ringa amfani da man kariya daga rana idan za'a fita. 8. A sami isashshen bacci atleast 8 hours kullum. 9. A ringa yawan shan fruits da suke da vitamin C kamar irin su papaya, orange, banana, mango etc da vegetables like Carrot, Alayyahu, tomato. 🍅 10. A ringa shan natural fruit juice ko da once or twice a week ne, kamar irin su Orange juice, Lemon juice, Carrot juice, potato juice

Wa ya haifar da hargitsi a kasar Sudan?

Image
  Wa ya haifar da hargitsi a kasar Sudan? Tashin hankalin da ya abku a kasar Sudan a kwanakin nan ya ja hankalin mutanen duniya. Inda labaran da aka watsa suka nuna cewa wannan rikici ne da ake samu tsakanin shugabannin sojoji na tsagi daban daban. Sai dai idan an bi bahasin ainihin dalilin abkuwar lamarin, to, za a gano cewa, kasar Amurka da yadda take shisshigi a harkokin gidan kasar Sudan su ne suka haifar da yamutsi a kasar. Manyan jami’an da suke rikici da juna a wannan karo a kasar Sudan, wato Abdel al-Burhan, kwamandan rundunar sojojin kasar, da Mohamed Dagolo, madugun rundunar RSF, sun kwaci ikon mulki daga hannun Omar al-Bashir, tsohon shugaban kasar, ta hanyar aiwatar da juyin mulki a hadin gwiwarsu, a shekarar 2019, inda suka samu goyon baya daga kasar Amurka. Idan mun duba tarihin shisshigin kasar Amurka a kasar Sudan, za mu ga ya fara ne tun farkon mulkin shugaba Omar al-Bashir a Sudan, inda a farkon shekarun 1990, kasar Amurka ta gabatar da kara ga babban taron Majalisar

EFCC ta ce Akpabio ya kai kan sa hedikwatar hukumar a ranar 9 Ga Mayu.

Image
 Hukumar EFCC ta nemi Sanata Godswill Akpabio, kuma tsohon Ministan Harkokin Neja Delta, cewa ya bayyana domin ta bincike salwantar maƙudan kuɗaɗe a cikin aljifan sa. Akpabio, wanda sanata ne daga jihar Akwa Ibom, ya na a sahun gaban waɗanda yanzu haka ke takarar neman zama Shugaban Majalisar Dattawa. EFCC ta ce Akpabio ya kai kan sa hedikwatar hukumar a ranar 9 Ga Mayu. Sanarwar ta biyo bayan wata wasiƙa da aka aika wa lauyan sa Umeh Kalu tun a ranar 13 Ga Afrilu. Akpabio, wanda tsohon gwamnan Akwa Ibom ne, an gayyace shi a cikin watan Maris, amma sai lauyan sa Kalu ya rubuta wa EFCC wasiƙa a ranar 27 Ga Maris, ya ce Akpabio ba zai samu kai kan sa ofishin EFCC ba, saboda a ranar ya na da ganin likitan sa a ƙasar waje. A cikin wasiƙar dai lauyan ya ƙara yi wa EFCC bayanin cewa Akpabio na fama da ciwon limoniya, kuma zuciyar sa kan fuskanci tsaikon bugawa. Akpabio, inji lauyan sa ya na fama da matsalar yin numfashi yadda ya kamata, kuma ya na jin ciwo idan ya na numfashi, shaƙar iska na

Mason Greenwood ya shaidawa abokansa cewa ba zai sake bugawa Manchester United wasa ba. Sam baya farin ciki da yanayin kungiyar akansa

Image
 Mason Greenwood ya shaidawa abokansa cewa ba zai sake bugawa Manchester United wasa ba. Sam baya farin ciki da yanayin kungiyar akansa. Daga: [Fagen Wasanni]

Batun Dawo Da Tsohon Sarkin Kano, Wannan Hurumin Sabon Gwamna Ne, Amma Za Mu Iya Bada Shawarar Abinda Ya Kamata, Cewar Kwankwaso

Image
 Batun Dawo Da Tsohon Sarkin Kano, Wannan Hurumin Sabon Gwamna Ne, Amma Za Mu Iya Bada Shawarar Abinda Ya Kamata, Cewar Kwankwaso Tsohon Gwamnan jihar Kano Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi magana game da maganar shirin cire Sarkin Kano ko dawo da tsohon Sarkin Kano Khalifa Muhammad Sunusi ll. Kwankwaso ya bayyana haka ne a yayin tattaunawar sa da ɗan jarida Abdullahi Sadou, kan batun Sarautar Kano. An tambayi Kwankwaso kan shin da gaske ne sabon Gwamnan jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf zai cire Sarkin Kano tare da dawo da Khalifa Muhammad Sunusi ll. Kwankwaso yace dama tun lokacin da muke kamfen babu abinda muka faɗawa mutane illa mun tabbatar musu cewa duk ayyukan da muka dakko su lokacin muna Gwamnati, to idan aka rantsar da sabuwar Gwamnati za'a cigaba da shi. Kuma mu a matsayin mu na Dattawa na tafiya, za mu cigaba da basu shawarwari, domin suyi abinda ya dace. Mun yi ƙoƙari ba mu ce za mu cire Sarki ko za'a canja ba lokacin kamfen amma yanzu kaga dama ta samu, su wad

Sergio Ramos: "Ban damu da sai na lashe kyautar Ballon d'Or ba. Idan ina so in lashe kyautar mutum guda ɗaya, da na buga wasan tennis

Image
 Sergio Ramos: "Ban damu da sai na lashe kyautar Ballon d'Or ba. Idan ina so in lashe kyautar mutum guda ɗaya, da na buga wasan tennis

Jam'iyyar NNPP mai jiran gado a Kano ta zargi gwamnatin jihar mai barin gado da yin zagon ƙasa ga shirin miƙa mulki hannun sabuwar gwamnati.

 Ganduje na yi wa shirin miƙa mulki zagon ƙasa - NNPP Jam'iyyar NNPP mai jiran gado a Kano ta zargi gwamnatin jihar mai barin gado da yin zagon ƙasa ga shirin miƙa mulki hannun sabuwar gwamnati. A wani taron manema labarai a ranar Juma'a, shugaban kwamitin miƙa mulki na gwamna a jam'iyyar NNPP Dr Abdullahi Baffa Bichi ya yi zargin cewa gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje, da gangan tana kawo cikan ga shirin miƙa mulki. Ya ce gwamnatin ta bai wa jam'iyyar NNPP gurbi uku kawai a cikin kwamitin da aka kafa don miƙa mulki hannun sabuwar gwamnati. Bayan zaɓen 18 ga watan Mairis ne aka bayyana Abba Kabir Yusuf na jam'iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Kano, inda ya kayar da ɗan takarar jam'iyya mai ci ta APC a ƙarkashin gwamna Abdullahi Ganduje. Dr Baffa Bichi ya ce "mutanen jihar Kano sun cancanci samun shirin miƙa mulki da zai tafi salin alin ba tare da tangarɗa ba." Ya ce ba su amince da tsarin da gwamnatin ta gabatar musu na cewa ɓangarenta

Zamu bada kyautar kati ga duk wanda ya canki nawa za'a tashi wasa tsakanin Al-Nassr da Al-Raed

Image
 Zamu bada kyautar kati ga duk wanda ya canki nawa za'a tashi wasa tsakanin Al-Nassr da Al-Raed

HOTUNA: Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi sallar Juma'a tare da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a masallacin fadar shugabancin ƙasa

Image
 HOTUNA: Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya yi sallar Juma'a tare da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a masallacin fadar shugabancin ƙasa, Ado Rock.

A Hukumance: Ousmane Dembele da Andres Christensen sun dawo cikin tawagar kungiyar kwallon kafa ta Barcelona bayan jinyar rauni.

Image
 A Hukumance: Ousmane Dembele da Andres Christensen sun dawo cikin tawagar kungiyar kwallon kafa ta Barcelona bayan jinyar rauni. Daga: [Fagen Wasanni]

Shin zaki iya Auren shagwaɓaɓɓen Namiji🤣🤣

Image
 Shin zaki iya Auren shagwaɓaɓɓen Namiji🤣🤣

Cika-bakin da 'yan adawa suka yi ne ya ja musu faduwa zabe a 2023 in ji Shugaba Buhari na Najeriya.

Image
 Cika-bakin da 'yan adawa suka yi ne ya ja musu faduwa zabe a 2023 in ji Shugaba Buhari na Najeriya.  Kun amince ko kuna da ja?

Bellingham zai koma Real Madrid, Barca zata sayarda yan wasa 2, Gasar Laliga ta gagari sauran gasanni...Cikakkun Labaran shiga nan👇

Image
 Bellingham zai koma Real Madrid, Barca zata sayarda yan wasa 2, Gasar Laliga ta gagari sauran gasanni...Cikakkun Labaran shiga nan👇

Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya samu damar ɗinka rigar Ka'aba (Kiswa) yayin aikin Umara da ya je a watan Ramadan.

Image
 Zaɓaɓɓen Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya samu damar ɗinka rigar Ka'aba (Kiswa) yayin aikin Umara da ya je a watan Ramadan.  📸: @Kyusufabba

A Hukumance: Alejandro Garnacho ya sanya hannu kan sabon kwantiragin shekaru biyar da Manchester United.

Image
 A Hukumance: Alejandro Garnacho ya sanya hannu kan sabon kwantiragin shekaru biyar da Manchester United. Daga: [Fagen Wasanni]

Fede Valverde da Vinicius Junior sun dauki wankan 'yan gayu suna kallon kungiyar kwallon kwando ta Real Madrid.

Image
 Fede Valverde da Vinicius Junior sun dauki wankan 'yan gayu suna kallon kungiyar kwallon kwando ta Real Madrid. Daga: [Fagen Wasanni]